API

Tarihin Hausa Da Hausawa Na Asali

Kabilar Hausa na daga cikin manyan ƙabilu a Afirka ta Yamma, kuma tarihin su ya mamaye ƙarni da dama. Tasirin su yana da matuƙar muhimmanci a siyasa, tattalin arziki, da al’adun Kasashe  da dama a Nahiyar Afrika.


Al’ummar Hausa na zaune a Arewacin Najeriya, da wasu sassa na Nijar, Kamaru, Chadi, da Sudan. An san su da juriya, harkokin kasuwanci, ilimi, da mulki. 

Asalin su yana da tushe a tarihi na gaskiya da kuma tatsuniya. A cewar labarin baka na Hausa, tushen su yana da alaƙa da Bayajida, wani Balarabe dan sarkin Bagadaza wanda ya zo yankin Sahel. 



Ya isa birnin Daura, mafi tsufa cikin biranen Hausa, inda ya kashe macijiya mai girma wanda ta hana jama’a shan ruwa. A sakamakon haka, sarauniyar Daura ta aure shi, kuma zuriyarsa suka zama sarakunan manyan biranen Hausa guda bakwai, wato Hausa Bakwai. Wadannan birane sun hada da– Kano, Katsina, Zazzau (Zaria), Gobir, Daura, Rano, da Biram.


A tsawon lokaci, Hausawa sun kafa birane masu ci gaba, kowanne yana da sarki mai mulki. Wadannan birane sun bunƙasa ta hanyar kasuwanci, noma, da sana’ar ƙere-ƙere. 


A ƙarni na 14, sun rungumi addinin Musulunci, wanda aka shigo da shi ta hanyar kasuwancin da ke gudana a saharar Afirka da tasirin malamai daga Arewacin Afirka. Wannan lokaci ne da biranen Hausa suka zama cibiyoyin ilimi da mulkin Musulunci.

Daya daga cikin abubuwan da suka fi tasiri a tarihin Hausawa shine Jihadin Shehu Usman Ɗanfodiyo a shekarar 1804. 


Ya jagoranci yunkurin gyara addini wanda ya kifar da wasu daga cikin sarakunan Hausa da ake zargi da zalunci, inda ya kafa Daular Sakkwato, daya daga cikin manyan daulolin Musulunci a Afirka ta Yamma. A ƙarƙashin wannan daula, yankunan Hausa sun haɗu a ƙarƙashin mulkin Musulunci, kuma malamai, ‘yan kasuwa, da shugabanni sun sami matsayi mafi girma.


Daga cikin shahararrun shugabanni a wannan lokacin akwai Shehu Usman Ɗanfodiyo, malamin addini kuma gwarzon da ya kafa Daular Sakkwato. Muhammadu Bello, ɗan Shehu Usman Ɗanfodiyo, ya zama sarkin musulmi na farko kuma ya ƙarfafa mulkinsa. Da kuma Nana Asma’u, ‘yar Shehu Ɗanfodiyo, fitacciyar malama ce, marubuciya, kuma mai fafutukar ilimin mata a al’ummar Hausa.


Daular Sakkwato ta ci gaba da mulki har zuwa lokacin mulkin mallaka na Birtaniya a farkon ƙarni na 20. Har yanzu, Sarkin Musulmi na Sakkwato yana da matsayi mai girma a matsayin jagora na ruhaniya da gargajiya a tsakanin Hausawan Najeriya. 

A lokacin mulkin mallaka a shekarun 1900, Birtaniya ta mulki yankunan Hausa a ƙarƙashin mulki na bayan fage wato 'indirect rule'. Ma’aikatan mulkin mallaka sun ci gaba da aiki tare da sarakunan gargajiya na Hausa, amma daga baya sun tauye ikon su gaba ɗaya sa mulkin siyasa. Duk da haka, Hausawa sun ci gaba da taka muhimmiyar rawa a siyasar Najeriya.


Bayan samun ‘yancin kai a shekarar 1960, fitattun ‘yan siyasa Hausawa suka bayyana, sun kuma taka muhimmiyar rawa wajen tsara makomar ƙasa. Daga cikin shahararrun shugabanni akwai Sir Ahmadu Bello, Firimiyan Arewacin Najeriya kuma jagoran jam’iyyar NPC. Ya taka rawar gani wajen haɗa kan Arewa da ƙarfafa al’adun Hausa-Fulani. Haka kuma, Janar Murtala Muhammad ya kasance wani jarumi kuma mai hangen nesa a matsayin shugaban ƙasa, kafin a kashe shi a cikin juyin mulki. Shehu Shagari ya zama shugaban ƙasa na farko da aka zaɓa a mulkin farar hula a jamhuriya ta biyu. Muhammadu Buhari, tsohon shugaban soja daga 1983 zuwa 1985, ya sake dawowa a matsayin zababben shugaban ƙasa a mulkin farar hula daga 2015 zuwa 2023.


Hausawa sun ci gaba da zama ɗaya daga cikin ƙabilun da suka fi tasiri a Najeriya. Harshen su, Hausa, shine yare mafi yawan masu magana da shi a Afirka ta Yamma, wanda ya zama yaren kasuwanci a yankin Sahel. An san su da kyawawan al’adunsu, gini na gargajiya, waka, adabi, da bukukuwan al’ada kamar Durbar – babban biki da yake nuna bajintar mahaya dawakai a biranen Kano, Katsina, da Zaria.


Masana’antar shirya fina-finai ta Hausa, wato Kannywood, ita ce masana’antar fina-finai mafi girma a Najeriya a cikin yaruka na gida, inda ake samar da fina-finai da ke nuna al’adun Hausa, addinin Musulunci, da batutuwan zamani. 


A fagen siyasa, kasuwanci, da ilimi, Hausawa na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen cigaban Najeriya. Sarakunan gargajiya, kamar Sarkin Kano da Sultan na Sakkwato, suna da babbar daraja a matsayin masu riƙon gadon al’adu da addini.


Tarihin Hausawa cike yake da kasuwanci, ilimi, da shugabanci tun daga kafa birnin Daura, zuwa kafa Daular Sakkwato, har zuwa shugabannin zamani. A yau, tasirin su a fagen siyasa, al’adu, da kasuwanci yana da ƙarfi, yana tabbatar da cewa gado da ɗaukakarsu za su ci gaba har zuwa nan gaba.