Kaduna - Shugaban Majalisar Wakilai Dr Abbas Tajudeen, ya bayyana matukar bakin ciki game da rasuwar malamin addinin Musulunci mazaunin Zariya, Sheikh Usman Idris Kusfa, wanda aka fi sani da Rigi-Rigi.
Ya bayyana marigayi malamin Tijjaniya a matsayin sanannen shugaban addini, wanda ya yi amfani da ilimin da Allah Ya ba shi wajen yada addinin Musulunci, inda ya gina al'umma mai adalci a addini.
Shugaban Majalisar Wakilai Abbas ya yi addu'ar Allah Ya jikan marigayi Sheikh Usman Kusfa, yana mai cewa, "Allah Ya gafarta masa kurakuransa Ya kuma ba shi mafi kyawun matsayi a Jannatul Firdaus."
Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Usman Kusfa, wanda aka sani da hanyar koyarwa ta musamman, ya rasu a daren Lahadi a Kaduna, yana da shekaru 57.
- Hajara Balarabe
